Matakin gwamnatin Najeriya na dakatar da kafa makarnatun gaba da sakandare
Update: 2025-09-02
Description
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan mako ya duba matakin gwamnatin Najeriya na dakatar da kafa makarantun gaba da sakandare a fadin ƙasar har na tsawon shekaru 7, mataakin da ya biyo bayan wani zama da majalisar zartaswar ƙasar ta yi a ƙarƙashin jagorancin shugaba Bola Ahmed Tinubu. Majalisar ta ce babu amfanin kafa makarantun da ba za a samu abin da ake buƙata ba, a maimakon haka zai kyautu a inganta waɗanda ake da su.
Comments
In Channel




