DiscoverIlimi Hasken RayuwaRashin albashi na shafar aikin koyarwa a makarantu masu zaman kansu a Najeriya - Rahoto
Rashin albashi na shafar aikin koyarwa a makarantu masu zaman kansu a Najeriya - Rahoto

Rashin albashi na shafar aikin koyarwa a makarantu masu zaman kansu a Najeriya - Rahoto

Update: 2025-12-02
Share

Description

A wannan makon, shirin yayi dubi ne kan batun yadda har kawo yanzu ake samun malaman makaratu masu zaman kansu a Najeriya dake ɗaukar albashin Naira dubu 15 zuwa sama, maimakon mafi ƙaranci albashin naira dubu 70 da gwamnati ƙasar ta yi dokar biya.

Duk da irin kuɗaden da ake shatawa iyayen yara, har ta kai idan yaronka ba a biya mishi kuɗin makaranta ba, to kuwa za a kora maka shi gida, hakan be sanya sun inganta albashin malaman ba.

Makaranta mai zaman kanta mutum ke kafa ta ko haɗin gwiwa na wasu mutane domin taimakawa ko ba gudunmawa yayin da a wannan lokaci da dama sun mayar da ita matsayin kasuwanci, abin da masana ke ganin kenan akwai buƙatar Malamai su samu yanayi mai kyau da walwala wanda ta hakanne zasu samu ƙwarin gwiwa wajan bayar da ilimi mai nagarta.

Hauwa'u Adam dake koyarwa a wata Makarata dake yankin Jambulo a jihar Kanon Najeriya, ta sheda mana cewa saboda karatunta yakai matakin digiri ne ake biyanta Naira dubu 20, amma masu kwalin babbar difloma ta HND da NCE albashin daga dubu 17 ne zuwa 18

Masana da masu fashin baki na ganin cewa, gwamnatoci sun yi sakaci sosai, musamman ta hanyar sakarwa makarantu masu zaman kansu linzami suna abin da suka ga dama, idan kaji mahukunta na kai ruwa rana da su to kuwa baya wuce akan haraji ne.

Comments 
In Channel
loading
00:00
00:00
x

0.5x

0.8x

1.0x

1.25x

1.5x

2.0x

3.0x

Sleep Timer

Off

End of Episode

5 Minutes

10 Minutes

15 Minutes

30 Minutes

45 Minutes

60 Minutes

120 Minutes

Rashin albashi na shafar aikin koyarwa a makarantu masu zaman kansu a Najeriya - Rahoto

Rashin albashi na shafar aikin koyarwa a makarantu masu zaman kansu a Najeriya - Rahoto

RFI Hausa